Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris ya bada gudummawar naira miliyan N7 ga mutanen ƙauyen Kanzanna a gundumar Tilli dake ƙaramar hukumar Bunza domin rage raɗaɗin harin yan bindiga a yankin.
Idris ya sanar da bada tallafin ne a yayin ziyarar ta’aziyya garin bayan da harin yan bindiga suka kai inda suka kashe mutane uku.
Gwamnan ya jaddada aniyarsa gwamnatinsa na kare rayuka dukiyar al’umma.
“Mun zo ne mu miĆ™a saĆ™on ta’aziyyarmu kan abinda ya faru. Muna rokon Allah ya jikan waÉ—anda suka rasa rayukansu a harin ya kuma bawa iyalansu hakurin jure rashin da suka yi” a cewar gwamnan.
A yayin ziyarar gwamnan na tare da jami’an tsaro na hukumar DSS, sojoji, yan sanda,Civil Defence da kuma yan bijilante.
Ya kuma yin alkawarin bawa jami’an tsaro duk gudunmawar da suke bukata domin samar da tsaro a jihar.