Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya fara rabon buhunan shinkafa ga mazauna jihar.
Ya kara da cewa kimanin mutane 1060 ne za su amfana da wannan, inda ya jaddada cewa za a raba sauran kayan abinci kamar gero, masara da sauransu ga marasa galihu.
Gwamna Yusuf ya ci gaba da cewa gwamnati ta yi wani shiri da ya dace ta hanyar kafa kwamitoci daban-daban domin tabbatar da rarraba kayan abinci yadda ya kamata.
Ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da shirin bada tallafin noma da aka gudanar a Kano.
A cewar sa, matakin na da nufin rage tasirin cire tallafin man fetur.
Ya yi gargadin cewa duk wani jami’in gwamnati da aka samu yana son rai a aikin rabon kayan abinci, za a yi maganinsa yadda ya kamata.
Gwamnan ya ci gaba da bayanin cewa, za a baiwa nakasassu kulawa ta musamman a yayin da ake gudanar da aikin raba kayan agajin, da nufin tabbatar da cewa kayan abinci sun isa ga masu rauni a cikin al’umma.