[ad_1]
Gwamnan jihar Benue,Samuel Ortom ya fice daga jam’iyar APC inda ya koma jam’iyyar PDP mai adawa.
Gwamnan ya sanar da haka a wani taro da ya gudanar da sabbin shugabannin kananan hukumomin jihar da kuma kansilolinsu a gidan gwamnatin jihar dake Makurdi.
Ya ce tuni ya aike da takardarsa ta barin jam’iyar ga shugaban mazabarsa.
“A hukumance na fice daga jam’iyar APC zuwa PDP na gabatar da takardar fita ta ga shugaban jam’iya na mazabata,”ya ce.
“Shugaban mazabar da kuma sauran jagororin jam’iyar a mazabar sun nuna sha’awarsu ta biyo ni sabuwar jam’iyata.shekaruna sun yi matukar kadan na daina siyasa.”
Sauya shekar ta Ortom na zuwa ne kwanaki guda bayan da da aka tsige kakakin majalisar jihar,Terkimbi Ikyange.
[ad_2]