Gwamna Ortom ya fice daga jam’iyar PDP

[ad_1]








Gwamnan jihar Benue,Samuel Ortom ya fice daga jam’iyar APC inda ya koma jam’iyyar PDP mai adawa.

Gwamnan ya sanar da haka a wani taro da ya gudanar da sabbin shugabannin kananan hukumomin jihar da kuma kansilolinsu a gidan gwamnatin jihar dake Makurdi.

Ya ce tuni ya aike da takardarsa ta barin jam’iyar ga shugaban mazabarsa.

“A hukumance na fice daga jam’iyar APC zuwa PDP na gabatar da takardar fita ta ga shugaban jam’iya na mazabata,”ya ce.

“Shugaban mazabar da kuma sauran jagororin jam’iyar a mazabar sun nuna sha’awarsu ta biyo ni sabuwar jam’iyata.shekaruna sun yi matukar kadan na daina siyasa.”

Sauya shekar ta Ortom na zuwa ne kwanaki guda bayan da da aka tsige kakakin majalisar jihar,Terkimbi Ikyange.




[ad_2]

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...