Gwamanti Tarayya ta ƙaryata rahotannin da ke nuna cewa za a mayar da Legas babban birnin Najeriya

Fadar shugaban kasa ta musanta rade-radin da ake yi kan yunkuri na mayar da birnin tarayya zuwa Legas, inda ta jaddada cewa irin wannan ikirarin ba shi da tushe balle makama da siyasa.

Bayo Onanuga, mai ba da shawara na musamman kan yada labarai da dabarun shugaba Bola Tinubu, ya yi watsi da jita-jitan, ya kuma zargi masu yada su da rashin gaskiya da kabilanci.

Onanuga ya fayyace cewa mayar da hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta Najeriya (FAAN) zuwa Legas kwanan nan ba ya nufin wani yunkuri na mayar da babban birnin tarayya can, domin gyaran da FAAN ta yi wani mataki ne kawai na gudanarwa na daidaita inda take da cibiyar masana’antar sufurin jiragen sama a Legas.

Ya jaddada cewa matsayin Abuja a matsayin babban birnin kasar an kafa shi bisa doka kuma ba zai canza ba.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...