Guguwa ta yi ta’adi a Amurka da Asiya

Iyalai sun shiga tasku bayan zabtarewar kasar da guguwar ta haifar a Benguet

Gwamnan Jihar North Carolina a Amurka ya gargadi abinda ya kira karuwar barazanar da rai ke fuskanta, sakamakon ambaliyar da guguwar Florence ta haifar.

Tuni dai guguwar ta yi sanadin rayukan mutum 16.

Roy Cooper ya bukaci mutane su kauracewa tituna, tare da bayyana cewa ba a taba fuskantar irin wannan barazanar ta ambaliya ba.

”Ya ce wannan guguwa na sake zama barazana a North Karolayna, an fuskanci ambaliya har a yankunan da basu taba ambaliya ba, wannan yanayi na iya haifar da zabtarewar kasa.”

Guguwar da ke tafe da ruwa da iska mai karfin gaske ta shafi jihohin Carolina ta Arewa da Carolina ta kudu.

Daruruwan mutane aka ceto, yayin da dubbai suka fake a matsugunan gaggawa, yawancin yankunan kuma na fama da rashin wutan lantarki.


Mutane na gudun neman tsiri dag guguwa mai karfi irinta da ake fuskanta a Asiya

A yankunan Asiya ma, mahaukaciyar guguwar da aka lakabawa suna Mangkhut ta ratsa yankunan kudancin China na Guangdong da Hainan tafe da karfin iska mai gudun kilomita 160 a sa’a 1, da ruwan sama kamar da bakin kwarya.

Mahukuntan China sun kwashe mutane kusan miliyan biyu da rabi a yankin da ke makare da mutane da dawo da dubun-dubatan jiragen kamun kifi tashoshi kafin isowar guguwar a yammacin Lahadi.

An kuma rufe akasarin shagunan da ma’aikatun gwamnati.

Kafafen yada labaran kasar sun ce mutum biyu sun mutu.

Hakazalika guguwar ta ratsa Hong Kong, inda ta girgiza dogayen benaye da tarwatsa tagogi.

A arewacin Philippines ma gomman mutane suka rasa rayukansu, ciki har da masu hakar ma’adinai 30.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...