A yau ne ake sa ran Femi Gbajabiamila, tsohon kakakin majalisar wakilai zai yi murabus daga majalisar wakilai.
Domin karbar ragamar shugabancin ma’aikatan fadar shugaban kasa karkashin Bola Tinubu.
Ku tuna cewa an nada Gbajabiamila a matsayin babban hafsan ma’aikatan shugaba Tinubu a ranar 2 ga watan Yuni.
Bugu da kari, shugaban ya nada Sen. Ibrahim Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata da George Akume, tsohon ministan ayyuka na musamman a matsayin sakataren gwamnatin tarayya.