Gawuna bai taya Abba Kabir Murna Ba – Rabiu Sulaiman Bichi

A cigaba da shari’ar zaben gwamnan jihar Kano jami’in jam’iyar APC mai karbar sakamakon zaben gwamnan, Rabiu Sulaiman Bichi ya ce É—an takarar gwamna a Æ™arkashin jam’iyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna bai mika sakon murna ba ga abokin takararsa na jam’iyar NNPP, Engr Abba Kabir Yusuf bayan da aka bayyana sakamakon zaben.

Bichi wanda shi ne sheda na 31 da aka gabatar a gaban kotun sauraren karar zaben gwamnan Kano ya bayyana haka lokacin da yake amsa tambayoyi.

A yayin zaman kotun lauyan masu kara, Ofiong Ofiong (SAN) ya gabatar da sheda na 31 da kuma 32.

Sheda na 31, Rabiu Sulaiman Bichi wanda shi ne jami’in APC mai karbar sakamakon zaben a jawabin da yayi a rubuce ya kuma rantse a ranar 9 ga watan Afirilu ya ce ya mikawa hukumar INEC dukkanin suna yen wakilan jam’iyar.

Ya ce ya halarci taron manema labarai da jam’iyar ta gudanar kuma babu inda ya yaji Gawuna ya taya Abba Kabir Yusuf murna.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...