Fasinjoji da ma’aikata 62 sun mutu a wani hatsarin jirgin sama a Brazil

Wani jirgin saman fasinja ɗauke da mutane 62 ya faɗo a wajen birnin São Paulo dake ƙasar Brazil inda ya kashe dukkanin mutanen dake ciki.

Jirgin na ɗauke da fasinjoji 58 da ma’aikata 4 a lokacin da yayi hatsarin a ranar Juma’a kamar yadda  sanarwar da kamfanin jiragen saman Voepass ya fitar ta ce.

Wasu hoton bidiyo da suka karaɗe kafafen sadarwar zamani sun nuna jirgin nayin hajijiya a sama kafin ya rikito ƙasa.

Ma’aikatar Civil Defence ta Brazil ta ce jirgin ya rikioto kan gidaje da dama.

Hukumomin sun ce gida ɗaya ne ya lalace kuma babu wani migadanci da ya jikkata.

Tuni shugaban ƙasar Lula da Silva ya aika da saƙon ta’aziyarsa ga iyalan mutanen a hatsarin ya rutsa da su.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]