Faisal Maina Ya Tsere Zuwa Amurka-EFCC

VOA Hausa

Babban lauya mai shigar da kara na hukumar EFCC Mohammed Abubakar wanda ya ya bayyana haka a babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, yace Faisal Maina da ake tuhuma da aikata laifuka uku da suka jibinci halallata kudin haram, ya gudu zuwa Amurka ne daga Jamhuriyar Nijar.
Alkalin da ke sauraron karar Faisal ya umarci a kwace kaddarorin da dan majalisar wakilai Sani Dan-Galadima, ya gabatar a kotu lokacin da ya tsaya wa Faisal da yake neman beli. Dan majalisar ya amince ya ajiye Naira miliyan 60 da kotu ta bukata daga duk wanda ya amince zai tsayawa Faisal kafin a bada belinshi.
Koto tana kuma tuhumar mahaifin Faisal Abdulrasheed Maina da aikata laifuka 12 da suka danganci halarta kudaden haram.
Kamar dansa Faisal, Sau biyu Abdulrasheed Maina yana tserewa bayan da aka ba da belinsa. Ko a shekarar da ta gabata, sai da mahaifin Fascal Abdulrasheed Maina, ya tsere zuwa jamhuriyar Nijar da niyar kaucewa fuskantar hukumci, kafin hukumar EFCC ta tasa keyarshi zuwa Najeriya inda aka tsaurara matakan ganin bai sake arcewa ba.
yan-sanda-sun-mayar-da-abdulrasheed-maina-najeriya
kotu-ta-sa-a-rufe-abdulrasheed-maina-a-gidan-yari
yadda-abdulrasheed-maina-ya-yanke-jiki-ya-fadi-a-kotu

Abdulrasheed Maina
Abdulrasheed Maina

Abdulrasheed maina na fuskantar shari’ar da ke zarginsa da wawure kudaden ‘yan fansho lokacin da ya jagoranci wani kwamitin aiki da cikawa na shugaban kasa kan fansho.
A lokutan baya, wata Babbar Kotun Tarayya ta bada umarnin a tsare Sanata Ali Ndume wanda ya tsayawa Abdulrasheed maina, saboda ya gaza gabatar da tsohon shugaban tsohuwar hukumar kula da fansho ta Najeriya lokacin da ya tsallake beli ya fice daga Najeriya.

More News

Kar ku ɓata rayuwarku da shan miyagun ƙwayoyi, Aisha Buhari ta faɗa wa yara

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, a ranar Asabar, a Abuja, ta bukaci yara su kasance masu kishin kasa ta hanyar "kaucewa" shan kwayoyi. "Muna son...

Mun ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutu—Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 29 ga watan Mayun 2023 a matsayin ranar hutu a fadin kasar nan a hukumance. Matakin dai...

Buhari ya zagaya da Tinubu a cikin Villa

Yadda Shugaban Najeriya bai barin gado, Muhammadu Buhari, ya zagaya da Shugaba mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu, a cikin fadar shugaban kasa. Ranar Litinin...

Hoto:Kwankwaso Ya kaddamar da wasu ayyuka a Kaduna

Biyo bayan gayyatar da gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai ya yi masa tsohon gwamnan jihar Kano, Rabi'u Musa Kwankwaso ya kaddamar da wasu...