Faisal Maina Ya Tsere Zuwa Amurka-EFCC

VOA Hausa

Babban lauya mai shigar da kara na hukumar EFCC Mohammed Abubakar wanda ya ya bayyana haka a babbar kotun tarayya da ke zama a Abuja, yace Faisal Maina da ake tuhuma da aikata laifuka uku da suka jibinci halallata kudin haram, ya gudu zuwa Amurka ne daga Jamhuriyar Nijar.
Alkalin da ke sauraron karar Faisal ya umarci a kwace kaddarorin da dan majalisar wakilai Sani Dan-Galadima, ya gabatar a kotu lokacin da ya tsaya wa Faisal da yake neman beli. Dan majalisar ya amince ya ajiye Naira miliyan 60 da kotu ta bukata daga duk wanda ya amince zai tsayawa Faisal kafin a bada belinshi.
Koto tana kuma tuhumar mahaifin Faisal Abdulrasheed Maina da aikata laifuka 12 da suka danganci halarta kudaden haram.
Kamar dansa Faisal, Sau biyu Abdulrasheed Maina yana tserewa bayan da aka ba da belinsa. Ko a shekarar da ta gabata, sai da mahaifin Fascal Abdulrasheed Maina, ya tsere zuwa jamhuriyar Nijar da niyar kaucewa fuskantar hukumci, kafin hukumar EFCC ta tasa keyarshi zuwa Najeriya inda aka tsaurara matakan ganin bai sake arcewa ba.
yan-sanda-sun-mayar-da-abdulrasheed-maina-najeriya
kotu-ta-sa-a-rufe-abdulrasheed-maina-a-gidan-yari
yadda-abdulrasheed-maina-ya-yanke-jiki-ya-fadi-a-kotu

Abdulrasheed Maina
Abdulrasheed Maina

Abdulrasheed maina na fuskantar shari’ar da ke zarginsa da wawure kudaden ‘yan fansho lokacin da ya jagoranci wani kwamitin aiki da cikawa na shugaban kasa kan fansho.
A lokutan baya, wata Babbar Kotun Tarayya ta bada umarnin a tsare Sanata Ali Ndume wanda ya tsayawa Abdulrasheed maina, saboda ya gaza gabatar da tsohon shugaban tsohuwar hukumar kula da fansho ta Najeriya lokacin da ya tsallake beli ya fice daga Najeriya.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...