EndSARS: Muhimman abubuwan da suka faru a Najeriya a makon da ya gabata

Ga wasu daga cikin muhimman abubuwan da suka faru a makon da ya gabata – tun daga Lahadi 11 zuwa Asabar 17 ga watan Oktoban 2020.

An soke rundunar SARS a Najeriya, an kuma kafa SWAT

A makon da ya ya gabata ne Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Mohammed Adamu ya soke rundunar da ke yaƙi da fashi da makami a Najeriya wato SARS.

Ya bayyana hakan ne a wani jawabin kai-tsaye ga manema labarai a ranar Lahadin da ta gabata. Sai dai kwanaki kaɗan bayan soke rundunar ta SARS aka kafa wata mai suna Special Weapons and Tactics.

Tun da farko dai soke rundunar ta SARS ta biyo bayan zanga-zangar da aka shafe kwanaki ana yi a wasu jihohin Najeriya, inda ‘yan ƙasar ke zargin rundunar da kisa ba bisa ƙa’ida ba da cin zarafin da saɓa ƙa’idojin aiki.

Amma duk da ƙirƙiro sabuwar Rundunar SWAT da gwamnatin Najeriyar ta yi, ‘yan ƙasar na ci gaba da gudanar da zanga-zanga suna masu buƙatar sauyi a fannoni da dama na gudanar da gwamnatin ƙasar.

Rotimi Akeredolu na Jam’iyyar APC ya lashe zaɓen Ondo

A ranar Lahadi 11 ga wata, hukumar zaɓe ta Najeriya INEC ta sanar da Rotimi Akeredolu na Jam’iyyar APC a matsayin ɗan takarar da ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ondo da aka gudanar ranar Asabar.

Mista Akeredolu ya samu kuri’a 292,830, yayin da dan takarar jam’iyyar PDP, Mr Eyitayo Jegede yake biye masa da kuri’a 195,791, sai kuma dan takarar ZLP, Agboola Ajayi, wanda ya samu kuri’a 69,127.

Dukkanin ‘yan takarar uku lauyoyi ne kuma sun fito daga mazaɓun sanata uku daban-daban – Akeredolu daga Ondo ta Arewa; Jegede daga Ondo ta Tsakiya da kuma Ajayi daga Ondo ta Kudu.

Mista Akeredolu ne gwamnan da ke kan mulki a jihar tun shekarar 2016.

Matasa ɗauke da makamai sun tarwatsa ‘yan zanga-zanga a Abuja

Wasu matasa sun tarwatsa masu zanga-zangar #EndSars a shataletalen Berger da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Hotuna da bidiyo da aka yaɗa a shafukan zumunta sun nuna yadda matasan suka ɓullo daga wani wuri daban ɗauke da sanduna suna kai wa masu zanga-zangar hari.

Baya ga Abuja, an samu irin waɗannan matasan da suka tarwatsa irin wannan zanga-zangar a jihohin Filato da Legas da Edo.

A wani ɓangaren kuma, an tarwatsa zanga-zangar neman daƙile matsalar tsaro a arewacin Najeriya da aka gudanar a Jihar Kano ranar Alhamis.

Wasu tsageru ne rike da sanduna da adduna suka tarwatsa su a daidai titin Kabuga da ke ƙwaryar birnin na Kano tare da kwacen wayoyi.

Ganduje ya dakatar da mai ba shi shawara saboda sukar Buhari

A makon da ya gabata ne Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya dakatar da mataimakinsa na musamman kan kafafen yaɗa labarai, Salihu Tanko Yakasai kan wata suka da Salihun ya yi a shafin Twitter ga Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

A wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar a ranar Lahadi, ya ce umarnin na gwamnan zai fara aiki ne nan take.

A saƙon da Salihun ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya danganta Shugaban Najeriyar da “mara tausayi”, sai dai sa’o’i kaɗan ya goge wani ɓangare na saƙon da ya wallafa.

Salihu Yakasai na mayar da martani ne game da jan ƙafar da Buhari ya yi game da kiraye-kirayen da ‘yan Najeriya ke yi na rushe rundunar SARS ta ‘yan sanda sakamakon zargin cin zarafi da azabtarwa da ake zarginsu da yi.

Tattaunawar Ƙungiyar ASUU da Gwamnatin Najeriya

A ranar Alhamis da ta gabata ne Gwamnatin Najeriya ta tattauna da ƙungiyar malamai masu koyarwa na jami’o’i, inda da alama tattaunawar ta yi armashi.

Ana tunanin ɓangarorin biyu sun fahimci juna amma kuma hakan bai sa ɓangaren ƙungiyar malaman ya sanar da janye yakin aikin ba inda ƙungiyar ta sake amincewa su sake zama teburin tattaunawa da gwamnati.

Bayanai sun nuna cewa gwamnatin Najeriya ta amince ta biya ƙungiyar ta ASUU naira biliyan 30.

Sai dai kuma gwamnatin ba dukkanin kuɗin za ta bai wa jami’o’in ba, za ta dinga fitar da su ne kaɗan-ƙadan tsakanin watan Mayun 2021 zuwa Fabrairun 2022.

An shafe wata shida ɗaliban jami’o’i na zaman gida a Najeriya saboda yajin aikin na ASUU duk da ɗage dokar kulle da gwamnati ta yi.

More from this stream

Recomended