
Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati ta tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai kamar yadda wasu majiyoyi dake hukumar su ka tabbatar.
El-Rufai wanda jigo ne a jam’iyar adawa ta ADC ya mika kansa bisa ga EFCC a ranar Litinin biyo bayan gayyatar da ta yi masa domin ya amsa wasu tambayoyi.
A cewar majiyar dake hukumar tsohon gwamnan zai kwana a tsare a ofishin saboda rashin kammala tambayoyi da jami’an hukumar su ke yi masa.
” E yana tsare a hannun mu kuma zai kwana ne anan,” a cewar majiyar.
Majiyar ta kara da cewa za a iya sakin tsohon gwamnan a ranar Talata bayan an kara sa yi masa tambayoyi.
Tun da farko dai sai da jami’an yan sanda su ka yi artabua harabar hukumar da wasu masu zanga-zangar goyon bayan tsohon gwamnan.

