El-Rufai ya tunɓuke sarakuna biyu da kuma dagatai huɗu

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai ya amince da tsige sarakuna biyu a jihar.

Sarakunan da aka tsige sun haɗa da Mai Martaba Jonathan Paragua Zamuna na masarautar,Piriga da Mai Martaba Genaral Aliyu Ilyah Yamma na masarautar Arak.

Kwamishiniyar ƙananan hukumomi ta jihar, Hajiya Umma Ahmad ita ta bayyana haka cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.

A cewar sanarwar daga ranar Litinin sarakunan sun tashi daga matsayinsu.

Ana zargin Gen.Iliyah Yamma da laifin naɗa dagatai huɗu waɗanda ba sunansu gwamnatin jihar ta amince da su ba da kuma rashin zama a masarautar sa.

Shi kuwa Jonathan Damuna an cire shi ne daga mulki biyo bayan rikici da aka samu a masarautar sa tsakanin al’ummomin Gure da Kitimi dake masarautar ta Piriga dake karamar hukumar Lere.

Har ila sanarwa ta ce an cire dagatan ƙauyukan Aban, Abujan Mada da kuma Anji dake masarautar Arak.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...