El-Rufai Ya Sake Ganawa Da Jagororin Jam’iyar SDP

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasiru El-Rufai ya sake ganawa da wani jigon jam’iyar SDP inda hakan ya Æ™ara ruruta  raÉ—e-raÉ—in da ake na tsara makomarsa nan gaba a  siyasa.

An  nuna hoton El-Rufai a Abuja  gidan Sanata Abubakar Gada tare da shugaban jam’iyar SDP na Æ™asa, Shehu Gabam tare da wasu jagororin jam’iyar.

Karin waÉ—anda suke a wurin sun haÉ—a da Teslim Folarin wanda ya yiwa jam’iyar APC takarar gwamna a jihar Oyo a zaÉ“en 2023 da kuma Sanata Nazif Sulaiman jigo a jam’iyar PDP daga jihar Bauchi.

Taron ganawar na daren ranar Lahadi a gidan Sanata Gada na zuwa ne jim kaɗan bayan da El-Rufai ya gudanar da taron buɗa baki a gidansa dake Abuja da ya samu halartar mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro,Mallam Nuhu Ribadu da sauran wasu jiga-jigan ƴan siyasa.

A makon da ya wuce ne El-Rufai ya ziyarci Gabam a hedkwatar jam’iyar ta SDP.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...