![Nasiru El-Rufai](https://arewa.ng/storage/2020/09/EL-Rufai-ya-rattaba-hannu-kan-dokar-yi-wa-masu-fyade.jpg)
Asalin hoton, Facebook/Nasir el-Rufai
Gwamnan Jihar Kaduna Nasiru El-Rufai
Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya rattaba hannu kan dokar hukunci mai tsanani a kan duk wanda a ka kama da laifin fyade.
Dokar ta ba da damar kisa ko yin dandaka ga duk wanda a ka kama ya yi wa kananan yara ‘yan kasa da shekaru sha hudu fyade.
Hakama karkashin dokar za a iya yanke musu hukuncin daurin rai-da-rai.
Idan a ka kama mace kuwa dokar ta ce za a cire mata wani sashe na al’aura da ake kira Fallopian tube ko kuma a kashe ta.
Nasir el-Rufai ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa tabbas ya rattaba wa dokar hannu.
A makon da ya gabata ne majalisar jihar Kaduna ta amince da kudurin dokar.
Bugu da kari duk baligin da a ka kama da laifin yiwa ‘yan kasa da shekara 14 fyade, za a saka sunan shi kundin rajistar wadanda suka aikata fyade tare da wallafa su a kafafen yada labarai.
Kawo yanzu jihar Kaduna ce kawai a Najeriya da ta tanadi hukunci mai tsanani kan masu aikata fyade a Najeriya.
A na samun koke sosai kan fyade a watannin nan a Najeriya a yan watannin nan.
Kuma duk da hukumomi na samun nasarar kama masu aikata fyaden, ba kasafai a ke yanke musu hukunci ba.