EL-Rufai ya rattaba hannu kan dokar yi wa masu fyade dandaƙa

Nasiru El-Rufai

Bayanan hoto,
Gwamnan Jihar Kaduna Nasiru El-Rufai

Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya rattaba hannu kan dokar hukunci mai tsanani a kan duk wanda a ka kama da laifin fyade.

Dokar ta ba da damar kisa ko yin dandaka ga duk wanda a ka kama ya yi wa kananan yara ‘yan kasa da shekaru sha hudu fyade.

Hakama karkashin dokar za a iya yanke musu hukuncin daurin rai-da-rai.

Idan a ka kama mace kuwa dokar ta ce za a cire mata wani sashe na al’aura da ake kira Fallopian tube ko kuma a kashe ta.

Nasir el-Rufai ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa tabbas ya rattaba wa dokar hannu.

A makon da ya gabata ne majalisar jihar Kaduna ta amince da kudurin dokar.

Bugu da kari duk baligin da a ka kama da laifin yiwa ‘yan kasa da shekara 14 fyade, za a saka sunan shi kundin rajistar wadanda suka aikata fyade tare da wallafa su a kafafen yada labarai.

Kawo yanzu jihar Kaduna ce kawai a Najeriya da ta tanadi hukunci mai tsanani kan masu aikata fyade a Najeriya.

A na samun koke sosai kan fyade a watannin nan a Najeriya a yan watannin nan.

Kuma duk da hukumomi na samun nasarar kama masu aikata fyaden, ba kasafai a ke yanke musu hukunci ba.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...