EFCC ta sake  gurfanar da babban akanta na jihar Bauchi a gaban kotu

Hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta sake gurfanar da, Sirajo Jaja babban akanta na jihar Bauchi a gaban kotu kan zargin da ake masa da hannu a almundahanar kudaden da yawansu ya kai naira biliyan 1.48.

An gurfanar da Jaja a gaban mai shari’a, Obiora Egwuatu ta babbar kotun tarayya dake Abuja tare da Aliyu Abubakar wani mai canjin kudi da kuma kamfanin Jasfad Resources Enterprises.

Wadanda ake kara suna fuskantar tuhume-tuhume guda biyar da suka shafi almundahanar kudade, sata da kuma halarta kudin al’umma.

Tun da farko hukumar EFCC ta gurfanar da mutanen da ake kara a ranar 7 ga watan Afrilu  inda aka yi musu tuhume-tuhume 9 kan zargin almundahanar kudade da kuma karkatar da kudaden da yawansu ya kai naira biliyan 8.38.

Amma kuma yawan tuhumar da ake musu yanzu ya ragu da kuma yawan kudaden.

Wadanda ake karar sun musalta dukkanin tuhume-tuhumen da ake musu.

Lauyan wadanda ake kara Gordy Uche da Christ Uche sun nemi da kotun da ta sahalewa wadanda ake kara su cigaba da amfanar belin da kotun ta basu tunda farko.

Egwuatu ya dage shari’ar ya zuwa ranar 21 ga watan Yuli domin fara shari’ar.

More from this stream

Recomended