EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaÆ™i da masu yiwa tattalin arzikin Æ™asa ta’annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta.

A ranar Laraba, Michael Ohiare daraktan ofishin yaÉ—a labarai na tsohon gwamnan ya sanar da cewa Bello ya amsa gayyatar da hukumar EFCC ta yi masa kan zargin da ake masa na yin almubazzaranci da kuma aikata al-mundahanar kuÉ—aÉ—en da yawansu ya kai biliyan 82.

Michael ya ce Bello ya É—auki wannan matakin ne bayan da ya tattauna da iyalansa, abokanan siyasarsa da kuma tawagar lauyoyinsa.

Amma a wata sanarwa da hukumar ta fitar, Dele Oyewale mai magana da yawun EFCC ya ce har yanzu suna neman Yahaya Bello ruwa a jallo.

Oyewale ya ce maganganun da ake yaÉ—awa cewa Bello yana tsare a hannunsu ba gaskiya ba ne.

A ranar 18 ga watan Afrilu ne hukumar ta EFCC ta ayyana Bello a matsayin wanda ta ke nema ruwa-a-jallo bayan da ƙoƙarin kama shi ya gaza samun nasara.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...