
Jami’ai daga ofishin shiyarr Maiduguri na hukumar EFCC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati na sun kama wasu mutane uku da ake zargi da haƙar zinare ba bisa ka’ida ba.
An kama mutanen ne a garin Mallam Jakwa dake ƙaramar hukumar Hawul ta jihar Borno biyo bayan bayanan sirri da aka samu akan irin haramtaccen aikin da su ke aikatawa.
Mutanen da aka kama sun haɗa da Umar Muhammad, Modu Bamai Umar da kuma Sani Sama’ila.
Haramtaccen aikin hakar ma’adanai da su ke na jawo gurɓatar muhalli da kuma taɓarɓarewar tsaro a jihar .
Kayayyakin da aka samu tare da su sun haɗa da na’urar auna zinare da kuma wani zinare da suka haƙo.
Hukumar ta ce za a gurfanar da su a kotu nan bada jimawa.

