Duk wanda ya ce Najeriya kalau ta ke to a binciki kansa-Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matakin da yakamata ace ta kai ba a yanzu.

A cewar Obasanjo duk wanda ya ce komai na tafiya dai-dai a yanzu to yakamata a binciki kansa.

Obasanjo ya fadi haka ne ranar Laraba a wurin taron lakcar Gidauniyar Wilson Badejo karo na 15 a birnin Lagos.

“Nigeria ba ta kai inda yakamata ace ta kai a yanzu ba. Idan wani ya ce dai-dai ne a inda muke yanzu to kan sa na bukatar a duba shi” tsohon shugaban Ć™asar ya ce.

A cewar Obasanjo dole ne yan Najeriya su zabi É—an takara na gari a 2023 saboda cigaban kasar na tsaka mai wuya.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...