Dokar wa’azi ce za ta yi wa malamai linzami – Sheikh Daurawa

Sheikh Daurawa

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce ya kamata gwamnatocin arewacin Najeriya su fito da dokoki dangane da yadda ya kamata malamai na Musulunci da na Kiristanci yin wa’azi.

“Ni da ma ra’ayina tuntuni shi ne mu da muke wa’azi ya kamata a tantance mu shin mai wa’azi ya cancanta kuma yana da ilmi.”

Sheikh Daurawa ya kara da cewa “rashin tantance masu wa’azi ne ya sa ake samun rigingimun da ake ciki yanzu haka, inda za ka samu malami ya shiga gidan rediyo ya bude baki yana ta fadin abin da ya zo bakinsa.

Duk malamin da zai yi wa’azi da zage-zage to ba wa’azi yake ba ya zama dan tasha.”

Ya kamata idan akwai tsari to su kansu kafafen yada labarai za su bi wajen tantance wane malami kafin ma su nemi ya yi wa’azi.”

Sai dai Sheikh Aminu Daurawa ya nuna rashin jin dadinsa kan abin da ya ce rashin goyon bayan malamai dangane da wannan batu.

“Na sha yin irin wannan kiraye-kiraye na tsaftace harkar wa’azi amma ban samu goyon bayan malamai ‘yan uwana ba.”

‘Bara ba Musulunci ba ce’

Sheikh Aminu Daurawa ya ce kalmar ‘bara’ wadda ta samo asali daga kalamar Larabaci ‘Albarra’ da ke nufin mika hannu a karbi wani abu ‘ba musulunci ba ne’.

Ya ce idan ba da wani dalili na larura kamar sata ko gobara to shi ne aka yadda mutum zai iya neman taimako. Amma sabanin haka “ba musulunci ba ne.”

To sai dai Sheikh Daurawa ya dora laifin yin bara ga gwamnatoci inda ya ce “gazawar gwamnoni ce ta sa har yanzu ba iya samar da mafita ba dangane da batun yin bara da kuma karatun al’qur’ani.”

Ya kara da cewa ya kamata gwamnatoci su fahimci cewa ” akwai talauci a karkara abin da ke tilasta wa iyaye aikewa da ‘ya’aynsu zuwa birane. Saboda haka kokarin wayar da kai kadai ba zai amfani ba.”

Sheikh Daurawa ya kara da cewa duk da bai goyi bayan kyale jama’a musamman kananan yara su yi bara ba saboda ba musulunci ba ce amma “bai kamata a hana tsarin karatun al’qur’ani ba.”

Mayar da almajirai garuruwansu ba mafita ba ce

Sheikh Aminu Daurawa ya ce ba sa goyon bayan dibar almajirai a mayar da su garuruwansu na asali.

“Gazawar gwamnoni wajen tuntubar malaman addinin musulunci kan yadda ya kamata a zamanantar da tsarin karatun al’qur’ani ne yake kara jefa arewacin Najeriya cikin matsala.”

“An ce yanzu akwai almajirai milyan 9 a arewacin Najeriya, shin wane tanadi aka yi musu? Nawa ake ba su a kason arzikin Najeriya? Ka ga duk ba a ba su komai.”

Sheikh Daurawa ya ce mafita ita ce ” a duba yadda wasu kasashen musulmi ke tafiyar da tsarin karatun kur’ani domin a damfara shi.”

A karshe Daurawa ya ce ya kamata jama’a da gwamnatoci su fahimci banbanci tsakanin bara da karatun allo.

Ba cutar korona na yi ba

Fitaccen malamin ya kuma yi tsokaci kan ‘yar rashin lafiyar da ya yi a ‘yan kwanakin baya abin da ya sa aka daina jin duriyarsa.

“Da ma haka rayuwa take wata rana kana da lafiya wata rana ba ka da lafiya. rayuwa kullum cikin jarrabawa ake.

Hakika na samu jarrabawar rashin lafiya, inda na yi fama da Maleriya da Typhoid da kuma mura mai zafi.”

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...