Daraktan gidan tarihin Auschwitz ya buƙaci Buhari ya yafe wa yaron da ya zagi Allah a Kano

A team of Islamic Sharia enforcers called Hisbah is on patrol in the northern Nigerian city of Kano in an open pickup. File photo

Bayanan hoto,
Jami’an hukumar Hisbah a Kano

Daraktan kula da gidan tarihin Auschwitz, tsohon sansanin ƴan Nazi a Poland ya yi tayin zaman gidan yari na hukuncin ɗaurin shekara 10 da aka yanke wa wani yaro ɗan Najeriya mai shekara 13 da ya zagi Allah a Kano.

Dakta Piotr Cywinski, ya ce shi da wasu ƴan sa-kai 119 daga sassan duniya za su yi wa yaron zaman gidan yari na wata ɗaya ko wannensu.

A watan Agusta ne kotun shari’ar musulunci ta yanke wa yaron hukunci kan wasu kalamansa da ba su dace game da Allah yayin wata muhawara da abokinsa a jihar Kano

Lauyan yaron ya ɗaukaka ƙara, yana cewa hukuncin ya saɓa wa ƴancin yara da kuma kundin tsarin mulkin Najeriya. Ya shaida wa BBC cewa har yanzu ba a sa ranar sauraren ƙarar da ya ɗaukaka ba a kotun.

Jihar Kano na ɗaya daga cikin jihohi 12 a Najeriya da ke bin tsarin gwama shari’ar musulunci da dokokin ƙasa.

Asusun kula da yara ƙanana na Majalisar Ɗinkin Duniya Unicef, ya yi kira ga hukumomin Najeriya su gaggauta sake duba hukuncin.

Me daraktan gidan tarihin Auschwitz Memorial ya ce?

A cikin wasiƙar da ya aika wa Shugaba Buhari, Dakta Cywinski, ya rubuta cewa a shirye yake ya yi wa yaron zaman gidan yarin.

“Ba tare da la’akari da abin da ya faɗa ba, ba za a iya ɗaukar shi mai cikakken hankali ba, saboda shekarunsa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa idan har ba za a yafe wa yaron ba, shi da wasu ƴan sa-kai 119 za su yi masa zaman gidan yarin.

Ya kuma ce za su ɗauki nauyin karatun yaron.

Gidan tarihin na Auschwitz bai cika tsoma baki ba a irin wannan batu.

Zuwa yanzu gwamnatin Najeriya ba ta ce komi ba game da batun

Gidan tarihin na Auschwitz-Birkenau, tsohon sansaani ne na ƴan Nazi a Poland inda aka kashe mutum miliyan ɗaya da dubu ɗari ɗaya, kuma kusan mutum miliyan ɗaya da aka kashe Yahudawa ne.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...