Dan majalisar wakilai na jam’iyar LP ya koma APC

Chimaobi Atu, mamba a majalisar wakilai ta tarayya ya sauya sheka daga jam’iyar LP ya zuwa APC.

Shugaban majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas shi ne ya sanar da sauya shekar Atu  a zauren majalisar a yayin zamanta  na ranar Alhamis.

Atu na wakiltar mazabar Enugu north/south a majalisar.

Dan majalisar ya kara hujjar dalilin sauya shekar ta sa da rikici da yaki ci yaki cinyewa a cikin jam’iyar mai adawa inda ya ce hakan yana shafar yadda yake gudanar da aikinsa.

Ali Isa bulaliyar marasa rinjaye a majalisar ya kalubalanci sauya shekar inda ya bukaci a ayyana kujerar Atu a matsayin wacce babu kowa akanta bukatar da shugaban majalisar ya yi watsi da ita.

More from this stream

Recomended