Dalilin Da Ya Sa Ni Yin Tattaki Daga Legas Zuwa Abuja

[ad_1]

Jaridar Vanguard ta yanar gizo ta jiya Alhamis ta rubuta rahoton cewa wani mutum mai suna Malam Isa Muhammad Munlaila dan asalin jihar Borno dake adawa da sake tsayawar Shugaba Muhammad Buhari takara ya soma tafiya a kasa daga Lagos zuwa Abuja.

Isa Muhammad Munlaila ya dauki matakin ne a madadin matasan Nigeria da ya ce an yi masu alkawarin ayyuka da zara Buhari ya zama shugaban kasa. Saboda haka suka hada kai suka zabi shugaban, amma kaico, ya ba su kunya. Maimakon kirkiro ayyuka miliyan uku kamar yadda ya yi alkawari cikin shekaru uku abun da aka samu basu wuce 500,000 ba.

Malam Isa Muhammad Munlaila ya ce babu wanda ya zuga shi ko tunzura shi ya dauki matakin da ya dauka. Ya ce yana yi ne ba domin kudi ba, yana da nashi kudin. Kazalika ba ya cikin wata jam’iyyar siyasa. Yana wakiltar matasan Nigeria ne.

[ad_2]

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...