

A har kullum a kan samu yanayin da jagororin addini kan aikata wasu laifuka a matsayinsu na mutane. To sai dai kasancewar su jagorori a addini ya sa jama’a ke mamaki da shiga dimuwa idan mutanen da suka amince da su suka yi ba zata.
Batun yi wa mata musamman kananan yara da matasa fyade wani abu ne da ke ci gaba da ruruwa kamar wutar daji, inda a lokuta da dama a kan samu jagororin addini a irin wannan matsala.
Kwararru kan masu tabin hankali irin su Dakta Babagana Kundi Machina, Shugaban Asibitin Kwararru na jihar Yobe da ke birnin Damaturu, sun zayyana wasu dalilai guda biyu da suka ce su ne ke sa jagororin addini yin fyade.
Dakta Babagana Kundi Machina ya ce mafi yawancin lokaci wadanda aka yi wa fyade musamman mata kan fuskanci wasu matsaloli kamar haka:
Dakta Babagana ya bayar da shawarwari da ya kira matakan kariya kamar haka:
A karshen makonnan ne dai gomman masu fafutuka suka gudanar da zanga-zanga a Abuja da Legas na Najeriya da manufar bayyana wa mutane irin barnar da wasu fasto-fasto ke yi a majami’u.
An dai gudanar da zanga-zangar ne da manufar nema wa wata wadda ta yi zargin faston cocin Commonwealth of Zion Assembly COZA, Pastor Biodun Fatoyinbo da yi mata fyade.
To sai dai yayin da masu zanga-zangar ke kokarin goyon bayan Bisola Dakolo, a gefe guda an samu wasu masu zanga-zangar da ke goyon bayan Fasto Biodun Fatoyinbo.
Bisola Dakolo dai ta fito a wani bidiyo inda ta yi hira da wani dan jarida take sheda masa cewa Fasto Biodun ya yi mata fyade lokacin tana ‘yar shekara 16.
Ta kara da cewa ya yi mata fyaden ne fiye da sau daya, inda a karon farko faston ya yi lalata da ita a cikin gidansu da misalin karfe shida na safe.
Da aka tambaye ta dalilin da ya sa ba ta yi ihu ba domin jama’a su kai mata dauki sai ta ce “Ya rufe min baki.”
Bisola dai yanzu haka mai dakin fitaccen mawakin nan ce, Timi Dakolo kuma tana da yara.
Kwatsam bayan kammala ibadar ranar Lahadi, sai Fasto Biodun ya fito ya yi wa mahalarta cocin na sa jan kunne cewa ka da su shiga rikici saboda zargin lalata mata.
Ya kara da yin kira ga magoya baya da su zama masu zaman lafiya ka da su tayar da zaune tsaye.
Sai dai a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, faston ya ce sam bai taba yi wa wata mace fyade ba, inda ya yi barazanar kai Bisola gaban kuliya.
Ya kuma danganta ikirarin da wani yunkurin bata sunansa da na cocin.