Da wahala Arsenal ta sayi ‘yan wasa badi

Mikel Arteta
Image caption

Mikel Arteta

Dan wasan gaban Borussia Dortmund Jadon Sancho baya tunanin inda zai koma, duk da alakanta shi da komawa Manchester United ko Liverpool.(Mail).

Tottenham za ta nemi mai tsaron ragar Watford Ben Foster wanda yarjejeniyarsa da kungiyar za ta kare bana.(Sun).

Hakama Tottenham din na fatar ganin ta shiga gaban Roma wurin sayen mai tsaron bayan Manchester United Chris Smalling.

Yanzu haka Smalling mai shekaru 30 na zaman aro a Roma.(Calciomercato, in Italian).

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Smalling na zaman aro a Roma

Manchester United na sahun gaba cikin masu son sayen mai tsaron bayan Napoli na Italiya Kalidou Koulibaly.

Kungiyoyin Real Madrid da PSG hakama na neman dan kasar Senegal din mai shekaru 26.(Express, via Corriere dello Sport).

Mai horar da kungiyar Arsenal Mikel Arteta ba zai samu kudi mai yawa ba wurin sayen yan wasa, matsawar kungiyar ta kasa zuwa gasar zakarun turai a badi.

Rahotanni na cewa Arsenal ta kasa samun ribar azo a gani a bana.(Goal).

Shugaban kungiyar Inter Milan Giuseppe Moratta na tunanin ba za’a kammala kakar wasannin bana ba, in har ba’a samu mafita ba kan yaduwar cutar Coronavirus.

Mai horar da Manchester City Pep Guardiola ya ce ba za a iya ja da kungiyarsa ba idan ana maganar lashe kofunan cikin gida.

Hakan na zuwa bayan kammala wasan karshe na kofin Carabao inda City ta doke Aston Villa da ci 2-1 a filin Wembley. (BBC).

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...