Da gaske ne EFCC ta samu kudi a gidan Lawal Daura?

[ad_1]

Kudin da EFCC ta gano a Lagos a 2017

Hakkin mallakar hoto
Facebook/ EFCC

Image caption

Bankado kudaden da EFCC ta yi a Lago a watan Afrilu na 2017 ya ja hankalin ‘yan Najeriya a lokacin.

Ranar 7 ga watan Agusta ne dai mukaddashin shugaban Najeriya, Yemi Osinbajo ya kori Lawal Daura daga mukamin shugaban rundunar tsaro ta farin kaya (DSS) bayan jami’an hukumar sun hana sanatocin Najeriya shiga majalisa.

Mukaddashin shugaban kasar ya yi tir da aikin da ya bayyana cewa ya ci karo da tsarin mulkin Najeriya tare da shan alwashin ganowa da hukunta wadanda ke da hannu a aikin.

Da yammacin ranar ne dai Osinbajo ya gana da sabon shugaban hukumar da ya maye Daura, Matthew B. Seiyefa, da kuma shugaban hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon gasa, Ibrahim Magu.

Washe gari dai rahotanni sun ce jami’an hukumar EFCC sun kai samame gidan tsohon shugaban hukumar DSS, Ita Ekpeyong.

Bayan nan kuma aka fara yada wani bidiyo a shafukan sada zumunta wanda ake ikirarin cewar bidiyon kudin da aka samu a gidajen Tsohon shugaban DSS, Lawal Daura ne.

An yi ta yayata wani labari ma wanda yake ikirarin cewar an samu tsabar kudi naira biliyan 21 da da bindigogi 400 da kuma dubban katunan zabe na din-din-din a gidan Lawal Daura na Katsina.

Sai dai kuma binciken BBC ya gano cewar wannan bidiyon na kudaden da EFCC ta gano ne a wani gida daga cikin jerin gidaje masu alfarma da ake kira Osborne Towers a unguwar Ikoyi ta Legas.

Hakkin mallakar hoto
Facebook/EFCC

Image caption

Hukumar EFCC ta fitar da hotuna da bidiyo na aikin a wancan lokacin

Kuma a cikin watan Afrilun shekarar 2017 ne EFCC ta yi aikin wanda a yanzu ake ci gaba da yada bidiyon.

Bayan haka kuma hukumar DSS ta fitar da wata sanarwa inda ta ce bidiyon ba na gidan stohon shugabanta bane.

Hakzalika, sanarwar da kakkin hukumar DSS, Tony Opuiyo, ya fitar, ta ce ba gaskiya ba ne cewar an sami tsabar kudi Naira biliyan 21 da bindigogi 400 da kuma dubban katunan zabe na din-din-din a gidan Daura.

Yayata labaran karya dai na dada zama ruwan dare a kasashen duniya, musamman a lokutan zabe.

[ad_2]

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...