DA DUMI-DUMI | Sabbin jama’an Rundunar SWAT zasu fara daukar horo gobe Litinin – AREWA News

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya Muhammad Adamu ya bayyana cewa gobe Litinin za a soma horas da jami’an sabuwar rundunar SWAT da aka kafa wadda za ta maye gurbin SARS.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan ƙasar, Frank Mba ya fitar, ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa waɗanda za su kasance cikin sabuwar rundunar matasa ne masu jini a jika kuma dukansu sun shafe aƙalla shekara bakwai suna aikin ɗan sanda.

Hakazalika ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa ba su da wani tabo ko kuma tarihi na laifi da suka aikata a baya, ba kuma a taɓa samunsu da laifin take haƙƙin bil adama ba ko kuma saɓa ƙa’idar amfani da makami.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an da aka zaɓa suna da cikakkiyar lafiya da za su jure namijin horon da za a ba su.

Za dai a soma horas da ‘yan sandan ne a kwalejojin horas da ‘yan sanda ta Ila Oragun, da ke jihar Osun da kuma kwalejin horas da ‘yan sanda ta jihar Nasarawa

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...