DA DUMI-DUMI | Sabbin jama’an Rundunar SWAT zasu fara daukar horo gobe Litinin – AREWA News

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya Muhammad Adamu ya bayyana cewa gobe Litinin za a soma horas da jami’an sabuwar rundunar SWAT da aka kafa wadda za ta maye gurbin SARS.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan ƙasar, Frank Mba ya fitar, ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa waɗanda za su kasance cikin sabuwar rundunar matasa ne masu jini a jika kuma dukansu sun shafe aƙalla shekara bakwai suna aikin ɗan sanda.

Hakazalika ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa ba su da wani tabo ko kuma tarihi na laifi da suka aikata a baya, ba kuma a taɓa samunsu da laifin take haƙƙin bil adama ba ko kuma saɓa ƙa’idar amfani da makami.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an da aka zaɓa suna da cikakkiyar lafiya da za su jure namijin horon da za a ba su.

Za dai a soma horas da ‘yan sandan ne a kwalejojin horas da ‘yan sanda ta Ila Oragun, da ke jihar Osun da kuma kwalejin horas da ‘yan sanda ta jihar Nasarawa

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]