DA DUMI-DUMI | Sabbin jama’an Rundunar SWAT zasu fara daukar horo gobe Litinin – AREWA News

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya Muhammad Adamu ya bayyana cewa gobe Litinin za a soma horas da jami’an sabuwar rundunar SWAT da aka kafa wadda za ta maye gurbin SARS.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan ƙasar, Frank Mba ya fitar, ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa waɗanda za su kasance cikin sabuwar rundunar matasa ne masu jini a jika kuma dukansu sun shafe aƙalla shekara bakwai suna aikin ɗan sanda.

Hakazalika ya bayyana cewa jami’an da aka zaɓa ba su da wani tabo ko kuma tarihi na laifi da suka aikata a baya, ba kuma a taɓa samunsu da laifin take haƙƙin bil adama ba ko kuma saɓa ƙa’idar amfani da makami.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an da aka zaɓa suna da cikakkiyar lafiya da za su jure namijin horon da za a ba su.

Za dai a soma horas da ‘yan sandan ne a kwalejojin horas da ‘yan sanda ta Ila Oragun, da ke jihar Osun da kuma kwalejin horas da ‘yan sanda ta jihar Nasarawa

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...