[ad_1]
Kwamishinan Lafiya Na Jihar Kano, Dakta Kabiru Ibrahim Getso, a jiya ya bayyana cewa tsakanin watan Janairu zuwa na Yulin wannan shekara, annobar cutar kwalara ta kashe mutane 28 a kananan hukumomi 23 dake jihar.
Ya fadawa yan jarida cewa gwamnatin jihar ta amince da ware naira miliyan 33 domin kariya da kuma shawo kan cutar.
Kwamishinan ya kuma ce gwamnati ta samar da wasu matakai na kawo karshen annobar.
Ya ce shawo kan cutar ba nauyin gwamnatin jihar bane kaɗai nauyi ne na dukkanin masu ruwa da tsaki ciki har da kungiyoyin farar hula, yan jarida da kuma kungiyoyin al’umma.
[ad_2]