Coronavirus : Kasashen turai na ci gaba da dawo da matakan kullen korona

An bude wasu makarantu a turai

Kasashe a fadin Turai na tsaurara matakan kullen korona, sakamakon karuwar wadanda ke kamuwa da cutar cikin hanzari da ake samu a nahiyar.

Wani sabon tsari mai matakai uku ya fara aiki a Ingila, wanda ya raba kasar zuwa matakai uku, wuraren ake da barazanar yaduwar cutar, da wadanda ke da matsakaiciyar barazana da kuma wadanda ke da barazana sosai.

Masu bawa gwamnatin kasar shawara kan harkokin kimiyya sun ce tsarin ya yi sassauci sosai.

Netherlands ta sanar da kulle wani bangaren ta har nan da makwanni hudu masu zuwa, kana ta tilastawa jama’a yin amfani da takunkumi.

A jamhuriyyar Czech ma tuni aka soma sake rufe makarantu, wuraren shan barasa da kuma dandali har nan da makonni uku.

Ministan lafiyar kasar Roman Pry-mula, ya ce mutane da dama sun saki jiki sakamakon sassauta dokokin kulle a baya.

Kasashen Turai masu yawa sun bude iyakokinsu da makwabtansu na Tarayyar Turai bayan shafe watanni da aka kullesu kuma aka hana tafiye-tafiye saboda rage yaduwar annobar.

Hukumar gudanarwa ta Tarayyar Turai ce ta bukaci dukkan kasashen da ke cikin tarayyar da su kawo karshen matakan gaggawa da suka dauka, domin ta ce matakan ba su da tasirin da ake bukata saboda matakan bayar da tazara da kasashen suka fitar na cimma bukatun da ake da su na dakatar da bazuwar annobar.

Sai dai ana ganin janye matakan ya taimaka matuka gaya wajen sake samun yaduwar cutar a yanzu.

A wasu kasashen dai cutar na a kan matakin zagaye na uku a yanzu haka.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...