Cece-Kuce Akan Matsayin Nijar a Zaben Najeriya

Mawakan troupe Albishir, na jamhuriyar Nijar sun rera wakar kamfai ga dan takarar jam’iyyar APC a zaben shugaban kasar da za a gudanar a karshen mako a Najeriya, lamarin da tuni ya haifar da mahawara a yanzu haka a bisa yadda mawakan ke kwatanta wakar a matasyin wata gudunmawa daga shugaban kasar Nijar.

Muryar Amurka ta yi kokarin tuntubar jami’an kasar Nijar, domin jin abin da zasu ce kan wannan Magana, amma hakka bata cimma ruwa ba.

Wannan cece-kuce na faruwa ne kwanaki kalilan bayan da aka hango gwamnan jihar Zinder da na Maradi rataye da tutar APC a wuya a ya yin gangamin jam’iyyar na Kano, abin da ya janyo suka daga jam’iyyar adawa ta PDP wacce ke ganin an yi katsalandan.

Tuni dai kungiyoyi masu zaman kansu suka fara jan hankulan ‘yan Nijar a duk inda suke su nisanci kansu daga dukkan wani yunkurin shiga harakokin zabubukan da za a gudanar a ranar Asabar din da ke tafe a Najeriya don kaucewa fadawa tarkon ‘yan siyasa.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

More News

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya ɓuya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huɗu domin ya...

Ɗalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ɗalibai 9 aka tabbatar sun ɓace bayan da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Aƙalla mayaƙan Boko Haram biyu ne suka miƙa kansu ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai a yankin gabashin jihar Borno. Mayaƙan biyu...

Isa Dogonyaro Ɗan Majalisar Tarayya Daga Jihar Jigawa Ya Rasu

Isa Dogonyaro wakilin al'ummar ƙananan hukumomin Garki da Baɓura a majalisar wakilai ta tarayya ya rasu. Ɗaya daga cikin abokan aikin marigayin a majalisar tarayya,...