Burkina Faso ta sanya hannu da Rasha kan yarjejeniyar kan gina tashar wutar lantarki ta nukiliya

Shugaban mulkin soja na kasar Burkina Faso yasa ka hannu kan wata yarjejeniya da kasar Rasha ta gina tashar wutar lantarki ta makamashin nukiliya domin inganta samar da wutar lantarki a ƙasar.

Saka hannun na zuwa ne biyo bayan tattaunawa tsakanin Ibrahim Traore da shugaban kasar Russia Vladimir Putin a cikin watan Yuni a wurin taron kasashen Africa-Russia.

A wurin taron Traore ya roki ƙasar Rasha da ta gina tashar wutar lantarki ta nukiliya a kasar Burkina Faso wanda ya ce za ta taimaka wajen samar da wutar da kasar ke bukata.

Traore ya ƙwaci mulki ne a watan Satumba na shekarar 2022 kuma tuni ya mayar da hankali wajen kulla alaka da kasar Rasha domin samun tallafin tsaro da kuma na tattalin arziki.

More from this stream

Recomended