Buhari Ya Zabi Justice Ishaq Ya Wakilci Nigeria A ICC

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya zabi shugaban alkalin alkalai na birnin Abuja, Alkali Ishaq Usman a matsayin wanda zai wakilce Najeriya domin zama babban lauya a kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC).

Kotun wacce ta fara aiki ranar 1 ga watan Yulin shekarar 2002 a matsayin kotun kasa da kasa wacce ke birnin Hague na kasar Netherlands.

ICC na da ikon hukunta mutane da ake tuhuma da aikata laifukan yaki, da keta hakkin bil adama da cin zarafi da dai sauransu.

A ranar 7 zuwa 17 ga watan Disambar wannan shekarar ne ake sa ran gudanar da zaben mukamin.

Za a gudanar da zaben a hedikwatar majalisar dinkin duniya da ke birnin New York kuma za a zabi alkalai 6 wadanda zasu cika kashi daya na 3 na kotun.

Kafin yanzu, Hon. Ishaq Usman Bello ya yi aiki a kwamitoci da suka shaki shari’a daban daban.

Ya kuma yi muhimman ayyuka kamar wakiltar Najeriya a kotu da jagorantar zaman da suka shafi shari’ar zabe.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...