Buhari ya saka dokar hana fita ta mako biyu a Kano – AREWA News

Shugaban kasa Muhammad Buhari ya ayyana saka dokar zaman gida ta mako biyu a fadin Kano baki daya.

Buhari ya bayyana haka ne cikin jawabin da ya yi wa yan Najeriya ranar Litinin.

Shugaban kasar ya ce dokar hana fitar da ya saka a Kano ta mako biyu zata fara aiki ne nan take daga yau.

Ya ce a yayin da dokar take aiki gwamnatin tarayya za ta mayar da hankali kacokan kan jihar ta hanyar aikewa da jami’an kiwon lafiya dama kayan aiki domin ganin an shawo kan matsalar mace-macen dake faruwa a birnin.

An dai ta yin kiraye-kiraye kan gwamnatin tarayya ta kawowa jihar dauki kan halin da take ciki.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...