Buhari ya saka dokar hana fita ta mako biyu a Kano – AREWA News

Shugaban kasa Muhammad Buhari ya ayyana saka dokar zaman gida ta mako biyu a fadin Kano baki daya.

Buhari ya bayyana haka ne cikin jawabin da ya yi wa yan Najeriya ranar Litinin.

Shugaban kasar ya ce dokar hana fitar da ya saka a Kano ta mako biyu zata fara aiki ne nan take daga yau.

Ya ce a yayin da dokar take aiki gwamnatin tarayya za ta mayar da hankali kacokan kan jihar ta hanyar aikewa da jami’an kiwon lafiya dama kayan aiki domin ganin an shawo kan matsalar mace-macen dake faruwa a birnin.

An dai ta yin kiraye-kiraye kan gwamnatin tarayya ta kawowa jihar dauki kan halin da take ciki.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...