Buhari ya mayar wa Obasanjo da Atiku martani

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya mayar wa tsohon Shugaban kasar Olusegun Obasanjo martani game da nuna goyon bayansa ga Atiku Abubakar a zaben 2019.

A ranar Alhamis ne dan takarar shugabancin kasar a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya gana da Mista Obasanjo a gidansa da ke Abeokuta a jihar Ogun, inda rahotanni suka ce ya ce yana goyon bayan Atikun a zaben 2019.

Sai dai a wata sanarwa da mai taimaka wa Shugaba Buhari kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce ba su yi mamakin labarin da ke cewa “Obasanjo yana goyon bayan a Atiku a zaben 2019, dukansu ba za su yi nasara ba.

“Ba mu manta ba kuma ‘yan Najeriya su ma suna sane cewa kimanin shekara 11 da ta wuce ne tsohon shugaban da kuma tsohon mataimakinsa a kokarinsu na neman mulki suka zargi juna da aikata cin hanci da karbar rashawa,” in ji Malam Garba Shehu.

Atiku Abubakar ya wallafa hotunansa a shafinsa na Twitter tare da Obasanjo da malamin addinin Musulunci Dr Ahmad Gumi da malamin addinin Kirista Bishop Matthew Hassan Kuka.

Atiku Abubakar ne ya yi wa Olusegun Obasanjo mataimaki lokacin da yake shugaban najeriya tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007.

Tun bayan nan, dangantakar da ke tsakaninsu ta yi tsami kuma Obasanjo bai taba goyon bayan Atiku Abubakar ba a duk lokutan da ya fito a baya na nuna son yin shugabancin Najeriya.

An taba ruwaito Obasanjo yana cewa “zai yi iya bakin kokarinsa don ganin Atiku Abubakar bai shugabanci Najeriya ba.”

Sai dai a wata hira da BBC ta yi da Atiku Abubakar, ya ce “Obasanjo ba shi ne Allah ba, kuma ba shi ne mutanen Najeriya ba.”

Olusegun Obasanjo dai na daya daga cikin masu fada a ji a fagen siyasar Najeriya.

Kuma ya nuna goyon bayansa ga Shugaba Buhari a lokacin da ya lashe zaben 2015, sai dai a bana ya ce ba ya goyon bayan shugaban ya nemi wa’adi na biyu a zaben shekarar 2019.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...