Buhari Ya Kaddamar Da Kamfanin Taki Na Dangote A Legas

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya kaddamar da kamfanin sarrafa takin zamani mafi girma a duniya mallakar kamfanin Dangote.

Kamanin, wanda ke unguwan Lekki a jihar Legas wacce ke kudu maso yammacin Najeriya, zai rika sarrafa takin zamani samfurin Urea da Ammonia.

Ana kuma sa ran zai samar da tan miliyan 3 a shekara domin amfanin ciki da wajen Najeriya.

A jawabinsa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana kamfanin a matsayin abin alfahari wajen ci gaban tattalin arziki da saka jari a kasar.

Ya kuma yi kira ga sauran ‘yan kasuwan Najeriya da su yi koyi da shugaban kamfanin na Aliko Dangote wajen saka jari a cikin gida, domin samar da aikin yi da kuma gina kasa.

Masana tattalin arziki irinsu Dr. Dauda Mohammed Kontagora na cewa hakan zai iya samar da aikin yi da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

A bangarensa shugaban kamfanin Dangote, Aliko Dangote ya ce wannan kamfani zai samar da ayyukuan yi ga dubban matasan kasar da kuma sarrafa takin zamani domin amfanin manoman ciki da wajen kasar.

Bayan kaddamar da wannan katafaren kanfanin, har ila yau shugaba Buhari ya duba aikin gina sabon tashar jiragen ruwa domin rage cunkoso a tashar jiragen ruwa ta Tincan da Apapa da yanzu haka suka cunkushe kuma suke kawo tsaiko wajen hadahadar kasuwanci zuwa ciki da wajen Najeriya.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...