Buhari Ya Kaddamar Da Kamfanin Taki Na Dangote A Legas

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya kaddamar da kamfanin sarrafa takin zamani mafi girma a duniya mallakar kamfanin Dangote.

Kamanin, wanda ke unguwan Lekki a jihar Legas wacce ke kudu maso yammacin Najeriya, zai rika sarrafa takin zamani samfurin Urea da Ammonia.

Ana kuma sa ran zai samar da tan miliyan 3 a shekara domin amfanin ciki da wajen Najeriya.

A jawabinsa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana kamfanin a matsayin abin alfahari wajen ci gaban tattalin arziki da saka jari a kasar.

Ya kuma yi kira ga sauran ‘yan kasuwan Najeriya da su yi koyi da shugaban kamfanin na Aliko Dangote wajen saka jari a cikin gida, domin samar da aikin yi da kuma gina kasa.

Masana tattalin arziki irinsu Dr. Dauda Mohammed Kontagora na cewa hakan zai iya samar da aikin yi da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

A bangarensa shugaban kamfanin Dangote, Aliko Dangote ya ce wannan kamfani zai samar da ayyukuan yi ga dubban matasan kasar da kuma sarrafa takin zamani domin amfanin manoman ciki da wajen kasar.

Bayan kaddamar da wannan katafaren kanfanin, har ila yau shugaba Buhari ya duba aikin gina sabon tashar jiragen ruwa domin rage cunkoso a tashar jiragen ruwa ta Tincan da Apapa da yanzu haka suka cunkushe kuma suke kawo tsaiko wajen hadahadar kasuwanci zuwa ciki da wajen Najeriya.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...