[ad_1]
A daren yau Laraba shugaban kasa, Muhammad Buhari ya gana da yan majalisar dattawa da aka zaba karakashin jam’iyar APC mai mulki.
Ganawar da shugaban kasar ya yi da yan majalisar bata rasa nasaba da sauya shekar da wasu daga cikin yan jam’iyar ta APC su kayi.
Masana da dama na ganin sauya shekar da wasu daga cikin yan majalisar suka yi ka iya kawowa jam’iyar cikas a zaben shekarar 2019.
A baya dai shugaban ya sha nanata cewa ba zai tsoma baki ba akan rikicin dake faruwar a jam’iyar ta APC.
[ad_2]