
Shugaban kasa, Muhammad Buhari ya gana da gwamnan Babban Bankin Najeriya,Godwin Emefiele a fadar Aso Rock dake Abuja a ranar Litinin.
Wannan ne karo na uku da Buhari yake ganawa da Emefiele tun bayan da ƙarancin takardar kuɗin Naira ya ta’azzara a sassa daban-daban na Najeriya.
Bai yi magana da yan jaridu ba bayan ganawar.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa makasudin ganawar ta su bata rasa nasaba da kokarin da ake na shawo kan matsalar ƙarancin kuɗin da ya addabi ko ina.