Shahararren mawakin siyasar Hausa, Dauda Kahutu, wanda aka fi sani da Rarara, ya zargi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da mikawa shugaban kasa Bola Tinubu ƙasa a cikin mummunan yanayin tattalin arziki.
Rarara, wanda ya fito fili bayan ya fitar da wakoki da dama ga Buhari, ya kuma ce ya yi nadamar goyon bayan tsohon shugaban.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Alhamis.
Ya yi mamakin dalilin da ya sa har yanzu gwamnatin Tinubu ba ta bayyana ra’ayinsu game da sakaci da gwamnatin Buhari ta yi ba.
Mawakin ya kuma yi ikirarin cewa an hana shi damar ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu domin ba shi shawara kan yadda zai fallasa almundahana da gwamnatin da ta shude ta yi.