[ad_1]
Najeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro da Birtaniya don taimaka wa Shugaba Muhammadu Buhari yaki da Boko Haram.
An yi shelar wannan yarjejeniyar ne dai a lokacin da Firayim Minister Theres May ta kai ziyara Najeriya.
Wata sanarwa ta ce Birtaniya “za ta fadada tallafin kayan aiki da horaswa ga sojin Najeriya domin kare kansu daga ababen fashewa da ‘yan ta’adda ke danawa”.
Yakin Boko Haram, wanda aka fara a shekarar 2009, ya haddasa mutuwar sama da mutum 20,000 , tare da raba mutum miliyan biyu da gidajensu a arewa maso gabashin Najeriya.
- An kama mutum 57 a Lagos bisa zargin luwadi
- Theresa May: Za mu karfafa alaka da Najeriya bayan ficewa daga Turai
Firayim Ministar ta ce: “Mun jajirce wajen aiki tare da Najeriya domin yaki da ta’addanci da rage tashin hankali, da kuma aza harsashin daidatuwar lamura da kuma arzikin da za su amfane mu gaba daya nan gaba.”
Yarjejeniyar ta kuma kunshi wani sabon shiri na fan miliyan 13 don ilmantar da yara 100,000 wadanda tashin hankali ya katse musu karatu.
Shirin zai samar da kayayyakin karatu da horasa da malamai da kuma wuraren karatu masu tsaro.
Birtaniya za ta kuma taimaka wajen dabarun yaki da ta’addanci da za su taimaka wa Najriya dakile yadda ake samun sabbin mayaka ‘yan ta’adda.
Ga hotunan rattaba hannun a yarjejeniyoyin da aka yi daga fadar shugaban Najeriya:
[ad_2]