Birnin Lisbon zai iya karbar gasar Champions League

Estadio da Luz

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Watakila a yi amfani da filin Benfica mai suna Estadio da Luz wajen buga wasan karshe a gasar Champions League a bana

Watakila birnin Lisbon ya karbi bakuncin wasan karshe na Champions League na bana cikin watan Agusta, idan hukumar kwallon Turai ta amince.

Uefa na shirin dauke wasan karshe na Champions League da ya kamata a buga a Istanbul da aka tsara yi tun 30 ga watan Mayu, wanda aka sake masa fasali.

Haka kuma hukumar na son dauke karawar karshe a Europa League da aka so yi a Poland ranar 27 ga watan Mayu ta mai da shi zuwa Jamus.

Uefa na son buga wasan daf da na kusa da na karshe da na daf da karshe da na karshe a fili daya ba tare da ‘yan kallo ba.

Cikin watan Maris aka dakatar da wasannin cin kofin Zaakarun Turai saboda tsoron yada cutar korona.

Ranar 17 ga watan Yuni ne babban kwamitin amintattu na hukumar kwallon kafar Turai zai yanke hukunci.

Za a buga wasan karshe a gasar Champions League ranar 23 ga watan Agusta, yayin da za a karkare gasar kofin Europa League ranar 21 ga watan na Agusta.

Birnin Lisbon na Portugal yana da manyan filin wasa biyu da dukkan abubuwan da ake bukata wajen buga tamaula da kuma otal da zai dauki kungiyoyin takwas da za su kara a gasar.

An ci gaba da gasar kwallon kafa ta cin kofin Portugal ranar 3 ga watan Yuni an kuma dage dukkan dokar da gwamanti ta saka ta hana zirga-zirga a watannan saboda tsoron yada cutar korona.

Tun ranar 16 ga watan Yuni aka ci gaba da gasar Bundesliga ta Jamus ba ‘yan kallo kuma filin wasa da ke Gelsenkirchen da Cologne da Duisberg da kuma Dusseldorf za su iya karbar bakuncin Europa League.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...