Birnin Lisbon zai iya karbar gasar Champions League

Estadio da Luz

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Watakila a yi amfani da filin Benfica mai suna Estadio da Luz wajen buga wasan karshe a gasar Champions League a bana

Watakila birnin Lisbon ya karbi bakuncin wasan karshe na Champions League na bana cikin watan Agusta, idan hukumar kwallon Turai ta amince.

Uefa na shirin dauke wasan karshe na Champions League da ya kamata a buga a Istanbul da aka tsara yi tun 30 ga watan Mayu, wanda aka sake masa fasali.

Haka kuma hukumar na son dauke karawar karshe a Europa League da aka so yi a Poland ranar 27 ga watan Mayu ta mai da shi zuwa Jamus.

Uefa na son buga wasan daf da na kusa da na karshe da na daf da karshe da na karshe a fili daya ba tare da ‘yan kallo ba.

Cikin watan Maris aka dakatar da wasannin cin kofin Zaakarun Turai saboda tsoron yada cutar korona.

Ranar 17 ga watan Yuni ne babban kwamitin amintattu na hukumar kwallon kafar Turai zai yanke hukunci.

Za a buga wasan karshe a gasar Champions League ranar 23 ga watan Agusta, yayin da za a karkare gasar kofin Europa League ranar 21 ga watan na Agusta.

Birnin Lisbon na Portugal yana da manyan filin wasa biyu da dukkan abubuwan da ake bukata wajen buga tamaula da kuma otal da zai dauki kungiyoyin takwas da za su kara a gasar.

An ci gaba da gasar kwallon kafa ta cin kofin Portugal ranar 3 ga watan Yuni an kuma dage dukkan dokar da gwamanti ta saka ta hana zirga-zirga a watannan saboda tsoron yada cutar korona.

Tun ranar 16 ga watan Yuni aka ci gaba da gasar Bundesliga ta Jamus ba ‘yan kallo kuma filin wasa da ke Gelsenkirchen da Cologne da Duisberg da kuma Dusseldorf za su iya karbar bakuncin Europa League.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da Æ´an ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an Æ´an sanda da kuma sojoji suna É—aukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar Æ´an sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe É—an Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa HaÉ—in Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...