![](http://arewa.ng/wp-content/uploads/screenshot_20221025_112728_com3844223355403912043-810x1024.jpg)
Bankin raya kasashen musulmi ya shirya gina asibiti mai gado 300 a jihar Kaduna.
Shugaban bankin ne ya bayyana haka bayan wata ganawa da suka yi da ministar kudi ta Najeriya, Zainab Shamsuna Ahmad a Abuja.
Shugaban bankin, Muhammed Al Jasser shi ne ya bayyana haka bayan ganawar ta su da ministan cikin wani sako da ya wallafa a shafin bankin na Twitter.
Al Jasser ya ce za a samar da asibitin karkashin tsarin yarjejeniyar Murabaha.
Ya kara da cewa wannan wani bangare na taimakawa fannin kiwon lafiya a Najeriya.