Babu wanda ya isa ya kamani, ina aikin Allah ne – AREWA News

Shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau ya cika baki a wani sabon fefan bidiyo cewa baza a iya kama shi ba saboda yana aikin Allah kuma Shi zai cigaba da kare shi.

“Babu wanda ya isa ya kamani saboda ina aikin Allah ne. Shi zai kare ni kamar yadda yake kare masu aiki makamancin haka kuma suke neman kariyarsa,” Shekau ya fada a cikin wani fefan bidiyo na tsawon mintuna 30 da ya fitar a matsayin martani kan farautarsa da rundunar sojan Najeriya ta fara da shi da manyan kwamandodinsa.

“Ina da tabbacin Allah zai kare kwamandodi na.Dukkaninmu muna aikin Allah ne.”

A cikin fefan bidiyon anga Shekau yans zaune kewaye da mayakansa guda biyu a cikin wani karamin daki da bashi da fadi.

A ranar Laraba 11 ga watan Nuwamba ne rundunar sojan Najeriya ta sake fara sabuwar farautar Shekau tare da kwamandodinsa.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...