Ba za mu taɓa sulhu a da ƴan bindiga a Zamfara ba—in ji Gwamna Dauda Lawal

Daga Sabiu Abdullahi

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya jaddada alkawarin gwamnatinsa na cewa ba za ta taba yin sulhu da barayi domin samar da zaman lafiya ba.

Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin mataimakinsa Malam Mani Mumuni, wanda ya ce gwamnatinsu a shirye take ta yi maraba da duk wata jam’iyyar adawa don neman mafita da kuma kawo karshen rashin tsaro a jihar.

“Ba ni kadai ne Gwamnan PDP ba, amma ni ne Gwamna a Zamfara gaba daya, don haka kowa ya cire wariya daga gwamnatina” Ya kara da cewa hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan zabensa nasara ce ga dimokuradiyya da ci gaban al’ummar kasar gaba daya.

Dauda Lawal ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar, Malam Mani Mummuni, a wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishinsa da ke Gusau, babban birnin jihar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]