Daga Sabiu Abdullahi
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya jaddada alkawarin gwamnatinsa na cewa ba za ta taba yin sulhu da barayi domin samar da zaman lafiya ba.
Gwamnan wanda ya yi magana ta bakin mataimakinsa Malam Mani Mumuni, wanda ya ce gwamnatinsu a shirye take ta yi maraba da duk wata jam’iyyar adawa don neman mafita da kuma kawo karshen rashin tsaro a jihar.
“Ba ni kadai ne Gwamnan PDP ba, amma ni ne Gwamna a Zamfara gaba daya, don haka kowa ya cire wariya daga gwamnatina” Ya kara da cewa hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan zabensa nasara ce ga dimokuradiyya da ci gaban al’ummar kasar gaba daya.
Dauda Lawal ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar, Malam Mani Mummuni, a wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishinsa da ke Gusau, babban birnin jihar.