Ba Coronavirus Ba Ce Ke Kashe Mutane A Kano – Ganduje – AREWA News

A jiya Lahadi Gwamnatin Jihar Kano ta yi ribas kan matsayarta dangane da Yawaitar mutuwa da ake fama da ita a Jihar. Sai dai ta ce, ba Coronavirus ba ce ke kashe Jama’a.

Gwamnatin ta ce tuni Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya umurci Kwamishinan Lafiya da ya yi bincike mai zurfi kan wannan lamari na Yawaitar mutuwa da musabbabinta.

Matsayar ta Gwamnatin Kano tana kumshe ne a wata takardar manema Labarai da Kwamishinan Labarai na Jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar. Inda ya ce, ana tsaka da yin bincike kan lamarin.

Sai dai ya ce, sakamakon da suka fara samu ya yi nuni da cewa yawaitar mutuwar ba ta da alaka da Coronavirus.

Kwamishinan ya ce, daga rahotannin da suka samu daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar sun yi nuni da cewa mafi yawan matuwar suna aukuwa ne sakamakon hawan jini, ciwon siga, sankarau da kuma zazzabin cizon sauro.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata Ganduje ya karyata batun Yawaitar mutuwa a Jihar Kano, Inda ya ce farfagandar makaryata ce kawai.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...