Ba Coronavirus Ba Ce Ke Kashe Mutane A Kano – Ganduje – AREWA News

A jiya Lahadi Gwamnatin Jihar Kano ta yi ribas kan matsayarta dangane da Yawaitar mutuwa da ake fama da ita a Jihar. Sai dai ta ce, ba Coronavirus ba ce ke kashe Jama’a.

Gwamnatin ta ce tuni Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya umurci Kwamishinan Lafiya da ya yi bincike mai zurfi kan wannan lamari na Yawaitar mutuwa da musabbabinta.

Matsayar ta Gwamnatin Kano tana kumshe ne a wata takardar manema Labarai da Kwamishinan Labarai na Jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar. Inda ya ce, ana tsaka da yin bincike kan lamarin.

Sai dai ya ce, sakamakon da suka fara samu ya yi nuni da cewa yawaitar mutuwar ba ta da alaka da Coronavirus.

Kwamishinan ya ce, daga rahotannin da suka samu daga Ma’aikatar Lafiya ta Jihar sun yi nuni da cewa mafi yawan matuwar suna aukuwa ne sakamakon hawan jini, ciwon siga, sankarau da kuma zazzabin cizon sauro.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata Ganduje ya karyata batun Yawaitar mutuwa a Jihar Kano, Inda ya ce farfagandar makaryata ce kawai.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...