Atiku Ya Shilla Zuwa Kasashen Turai

Dantakarar shugaban kasa a jam’iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya yi balaguro zuwa kasashen Turai.

Hakan na zuwa ne kwana guda bayan da ya kaddamar da kunshin mutanen da za su jagoranci yakin neman zaben sa.

Mr Paul Ibe mai bashi shawara kan kafafen yada labarai a cikin wata sanawa da ya fitar ya ce tafiyar ta Atiku bata da alaka da batun ganin likita domin a duba shi kamar yadda wasu suke yadawa.

“Da yammacin yau Atiku zai ta fi kasashen Turai domin kasuwanci” A cewar Ibe.

Har ila yau ya ce Atiku zai biya Dubai domin ganawa da wasu daga cikin iyalansa.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...