APC ta lashe zaben gwamnan Bayelsa, na Kogi ‘bai kammalu ba’ | BBC Hausa

Zauren da aka bayana sakamakon zaben gwamnan Bayelsa
Image caption

Zauren da aka bayana sakamakon zaben gwamnan Bayelsa

Hukumar zabe a jihar Bayelsa ta bayyana David Lyon na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben jihar.

Mr Lyon ya samu kuri’u 352,552 da suka ba shi damar doke sauran yan takara da suka hada da Mista Duoye Diri na jam’iyyar PDP wanda ya zo na biyu da kuri’u 143,172.

To amma Mista Diri dai ya yi fatali da sakamakon tun ma a lokacin da ake tattara shi.

Yadda ta kaya a jihar Kogi

A jihar Kogi hukumar zaben ta ce zaben Sanata da akayi a Kogi ta Yamma bai kammalu ba, kasancewar kuri’un da aka soke sunfi yawan wadanda wanda ke kan gaba ya bada tazara.

Smart Adeyemi na jam’iyyar APC ke kan gaba da kuri’u 80,118, yayin da mai bin sa Dino Melaye na jam’iyyar PDP ke da kuri’u 59,548.

To sai dai tun kafin bayyan sakamakon Mista Melaye yayi watsi da sakamakon da ake tattarawa.

A yanzu hukumar ta ce za ta saka lokacin da za ta gudanar da zaben cike gibi.

A wata mai kama da haka kungiyoyin da ke sa ido kan zaben sun yi watsi da sakamakon da aka tattara na zaben gwamna da sanata, inda suka ce an tabka kura-kurai.

An dai samu rikici a zaben jihar ta Kogi wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane uku ranar Asabar.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...