APC Ta Dage Taron Kwamitin Zartarwar Jam’iyar

Jam’iyar APC ta dage taron shugabanninta da kuma na kwamitin zartarwar jam’iyar.

Abubakar Kyari, shugaban rikon jam’iyar shi ne ya fadawa manema labarai haka bayan wani taron gaggawa na shugabannin jam’iyar na kasa a ranar Litinin.

Taron shugabannin da aka yi a hedikwatar jam’iyar dake Abuja an kira shi ne biyo bayan murabus ɗin shugabanta, Abdullahi Adamu da kuma sakataren jam’iyar, Iyiola Omisore.

Kyari ya ce canjin shugabanci da aka samu a jam’iyar shi ne dalilin dage taron.

Shugaban rikon jam’iyar ya ce nan gaba kadan za a sanar da ranar taron.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]