APC Ta Dage Taron Kwamitin Zartarwar Jam’iyar

Jam’iyar APC ta dage taron shugabanninta da kuma na kwamitin zartarwar jam’iyar.

Abubakar Kyari, shugaban rikon jam’iyar shi ne ya fadawa manema labarai haka bayan wani taron gaggawa na shugabannin jam’iyar na kasa a ranar Litinin.

Taron shugabannin da aka yi a hedikwatar jam’iyar dake Abuja an kira shi ne biyo bayan murabus ɗin shugabanta, Abdullahi Adamu da kuma sakataren jam’iyar, Iyiola Omisore.

Kyari ya ce canjin shugabanci da aka samu a jam’iyar shi ne dalilin dage taron.

Shugaban rikon jam’iyar ya ce nan gaba kadan za a sanar da ranar taron.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]